SHENZHEN, China – Wani dan kasar China da aka samu da laifin kashe wani yaro dan makaranta a Japan a watan Satumba na bara, an yanke masa hukuncin kisa a ranar 24 ga Janairu, 2025. Yaron dan shekara 10 ya rasu ne bayan wani harin wuka da aka kai masa a hanyarsa ta zuwa makaranta a birnin Shenzhen.
Hukuncin ya zo ne kwana guda bayan yankewa wani dan China makamancin wannan hukunci kan kai harin wuka a wata motar makaranta a birnin Suzhou. A lokacin harin, wata mata ‘yar China ta rasa ranta a kokarin kare fasinjoji ‘yan Japan da aka yi kokarin kashewa. Dukkanin laifuka biyu sun girgiza ‘yan Japan mazauna China.
Mahukunta Taliban a Afghanistan sun yi alla-wadai da bukatar sammacin kama shugabanninta, da aka gabatar a kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ICC, wanda suke cewa siyasa ce kawai. Ma’aikatar ketaren Taliban ta ce wannan wani shiri ne mara alkibila da adalci a cikinsa.
A jiya Alhamis, babban mai gabatar da kara a Kotun ICC, Karim Khan ya nemi kotu ta bada sammacin kama jagoran Taliban, Haibatullah Akhundzada da babban mai shari’a Abdulkarim Haqqani kan cin zarafi mata, manya da kanana.
Do you have a news tip for NNN? Please email us at editor@nnn.ng