Gwamnan jihar Kano, Abba Yusuf, ya jaddada goyon bayansa ga jihar Borno sakamakon ambaliyar ruwa da ta mamaye Maiduguri. A wata sanarwa da ya fitar, Gwamna Abba Yusuf ya bayar da tallafin N100m don taimakawa wadanda ambaliyar ta shafa.
Ambaliyar ruwa ta yi sanadiyar lalacewar gidaje da kayayyaki a Maiduguri, inda yawan jama’a suka rasa matsuguni. Gwamnatin jihar Borno ta bukaci jama’a su gaggauta tashi daga unguwannin da ambaliyar ta fi muni.
Wannan ambaliya ta zama daya daga cikin mafi muni da jihar ta gani cikin shekara 30, tun bayan madatsar ta Alau ta balle a watan Satumban shekarar 1994.
Ma’aikatan lafiya sun yi gargadin akwai yiwuwar barkewar cututtuka a Maiduguri sakamakon gurbacewar ruwan sha da kayan abinci.