Kanun Labarai
Guguwar iska ta lalata gidaje 327 a Cross River
A kalla gidaje 327 ne guguwar iska ta lalata a kauyukan Nkarasi da Abinti da ke karamar hukumar Ikom a jihar Cross River.
Godwin Tepikor, Ko’odinetan shiyyar Kudu-maso-Kudu na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Kasa, NEMA, a ranar Alhamis, ya jagoranci tawagar jami’an hukumar domin tantance irin barnar da aka yi.
Ma’aikatan Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Kuros Riba, SEMA, su ma sun je rangadin tantancewar.
Shugaban matasan yankin Nkarasi Pius Ayum ne ya jagoranci tawagar zagayen gidajen da abin ya shafa.
Mista Ayum ya ce guguwar ta afku ne a daren ranar 3 ga watan Maris tare da wata iska mai karfin gaske kafin ruwan sama mai yawa.
Mista Ayum ya ce guguwar ta lalata gidaje da itatuwan tattalin arziki a yankunan da lamarin ya shafa.
A cewarsa, bala’in ya jawo wa wadanda abin ya shafa wahala, ya kuma yi kira ga NEMA, SEMA da sauran hukumomin da abin ya shafa da su kawo musu dauki.
A yankin Abinti, wani basaraken gargajiya, Akeng Nelson ne ya jagoranci tawagar zagayen yankin.
Yayin da yake gudanar da tawagar, Nelson ya ce galibin gidaje sun kaura daga gidajen kakanninsu saboda rugujewar da ya sa akasarin rufin ke zubewa.
NAN