Kanun Labarai
2023: Za mu mara wa Tinubu baya saboda ya taimaka mana lokacin da yake Gwamnan Legas – Miyetti-Allah

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah, MACBAN, ta bayyana goyon bayansu ga jagoran jam’iyyar APC na kasa, Bola Tinubu, kan kudirinsa na tsayawa takara a zaben 2023.
Shugabannin Fulanin sun bayyana haka ne bayan taron da suka yi a cibiyar horas da aikin gona da kula da karkara da ke Abuja ranar Lahadi.
Taron dai ya samu halartar shugabannin Fulani daga jihohi 36 da kuma babban birnin tarayya Abuja.
Jagoran taron kuma wanda ya taba shugaban kungiyar MACBAN reshen Jigawa, Ya’u Haruna ya bayyana cewa a yanzu haka ana wayar da kan al’ummar Fulani kan zaben 2023, kan tsaro da yadda za su zauna lafiya da kansu da makwabta.
Ya ce: “Mafi yawan wuraren kiwo da muke da su, masu rike da madafun iko ne suka karbe su, don mu dawo da su, mu ma mu shiga siyasa har ma mu tsaya takara.
“Tuni da kuma bin kokarin da muka yi na wayar da kan jama’armu, yanzu da dama sun mallaki katin zabe, kuma suna jiran lokacin zabe ne kawai.
“Muna duba mutanen da ke nuna sha’awar tsayawa takarar shugaban kasa tare da Bola Tinubu, domin shi ne ya sa baki a lamarinmu a lokacin da yake gwamnan Legas kuma muka samu rikici a Benuwai.
“Tinubu ya zo gaba daya, ya dora mu a kan teburi kuma ya sulhunta mu, don haka, wanda zai iya yin haka a wancan lokacin, mun yi imanin zai iya yin fiye da haka idan yana kan jagorancin al’amura,” in ji Mista Haruna.
Shugaban na MACBAN ya koka da yadda ake ganin da yawa daga cikin Fulanin da ake tonowa a Najeriya a matsayin masu laifi duk da cewa da yawa ba su yi ba.
“Ba mu ce ko kadan ba mu ce babu masu aikata laifukan da ke yin garkuwa da mutane, satar shanu, fashi da makami da sauran laifuffuka ba, amma kuma dole ne a san cewa kaso mafi yawa na mutanenmu suna rayuwa cikin kwanciyar hankali da gudanar da sana’o’insu na halal.
“Muna son hada gwiwa da gwamnatin tarayya, gwamnatocin jihohi da kungiyoyin bayar da agaji na kasashen waje domin kafa makarantu domin matasan mu su samu ilimi da kuma amfani da iliminsu wajen amfani da su domin amfanin kasa,” inji shi.
Ya kuma ba da tabbacin cewa za a ci gaba da tuntubar Fulani domin ganin an samu zaman lafiya sosai, kuma an yi wa ’yan kabilarsa mutuncin da ya kamace su.
NAN